HAUSA NEWS

Kotu Ta Sake cin tarar hukumar KAROTA

Kotu Ta Sake cin tarar hukumar KAROTA

Kotu Ta Sake cin tarar hukumar KAROTA.

Babbar kotun jiha mai lamba 15 karkashin mai shari’a Nasiru Saminu ta yi watsi da bukatar hukumar KAROTA na ta dakatar da aiwatar da hukuncin hana goyon babur mai kafa biyu.

A zaman kotun na yau, mai shari’a Nasiru Saminu ya ki amincewa da bukatar ta su, inda kuma ya yankewa hukumar ta KAROTA tarar naira dubu goma bisa bata mata lokaci.

Tun da fari dai kotun ta bukaci hukumar KAROTA da ta biya tarar naira miliyan daya da dubu dari shida ga wasu mutum biyu da suka yi zargin cewa jami’an hukumar sun kama su a kan laifin yin goyo.

Guda daga cikin masu shigar da kara Kwamared Bello Basi ya tabbatarwa da Freedom Radio cewa, kotun ta saurari bukatar hukumar KAROTA, sai dai bayan nazari ta yi watsi da bukatarsu, ta kuma ci tarar su naira dubu goma.

SOURCE: PREEDOM RADIO KANO

360hausa Team

360Hausa is a current Best Hausa Entertainment blog in Africa that specialized in providing you high quality content. 360Hausa was found and manage by Abubakar Yusuf Radda (B2 [D Promoter] Slayer). A Blogger, Ghost Writer & Content creator. Follow us on Social Media @360Hausa

WHAT CAN YOU SAY ABOUT THIS ?

This site uses Akismet to reduce spam. Learn how your comment data is processed.

Back to top button