Shahararren Mawaki Hamisu Breaker Zai Fito A Cikin Sabon Kannywood Film Mai Suna “LULU DA ANDALU”.
Wannan Tabbas Babban Shiri Ne Wanda Ake Kashe Ma’Uden Kudade, Kuma Ake Warware Basira A Cikinsa.
Babban Mawakin Na Hausa Ya Shiga Cikin Shirin Ne, a Matsayin Mawaki Wanda Aka Gayyata. Inda Ya Rera Sabuwar Wakarsa SO (LOVE).
Mawakin Yayi Reposting Kamar Haka:
https://www.instagram.com/tv/CbGQ4JtDYsV/?utm_medium=copy_link
Wajen dauka Shirin series film din Lulu da Andalu
Ga LULU Ga ANDALU
Bismillahir rahmanir rahim!!!
MANSA MUSA wani shaharerren mai dukiya ne daga kasar MALI wanda tarihi ya tabbatar da cewa ya taba zama mutumin da babu wanda ya kaishi dukiya a duniya, yayi mulkinsa a matsayin MANSA na MALI tsakanin shekara ta 1312 sannan ya rasu ne a shekara ta 1337.
Sai kuma kwatsam a wannan zamani namu na shekara 2022 aka sami wani bawan Allah wanda burinsa shine ya gano inda dukiyar MANSA MUSA take domin ya mallaketa, amma domin gano inda dukiyar MANSA MUSA take dole sai an taso da wasu hatsabiban Aljanu guda biyu wato LULU da ANDALU daga dogon barcinsu na shekaru sama da 700 da suka gabata.
TAMBAYA
Shin wadannan aljanu da su kadai suka san inda dukiyar nan take za’a iya taso da su kuwa?
Shin in anyi nasarar tashinsu daga dogon barcinsu zasu bayyanar da inda dukiyar MANSA MUSA take kuwa?
Shin in anyi nasarar taso da LULU da ANDALU ya rayuwa zata kasance?
Shin waye ne wannan bawan Allah da yakeson mallakar dukiyar MANSA MUSA?
Ku biyumu cikin wannan shiri Mai dogon zango da ya hada soyayya,tashin hankali, kauna, kishi, kudiri, juriya, jarumta, hatsabibanci, Amana da yaudara.
LULU DA ANDALU
Tabbas wannan series din zaizo da abubuwan gani, burgewa, nishadantarwa da darasi abin kwaikwayo.
A film by @dan_hausa1
Created and produced by @official_tyshaban
Co-Produced by: @binisah1
Gaffer by @gaffergata
Make-up @sojimakeup
DOP @jimohfilms