Labari Da Dumi Duminsa, Yan Bindiga Sunyi Juyin Mulki, a Wasu Kauyukan Jahar Sokoto Nigeria.
Ɗan bindiga Bello Turji da yaranshi sunyi juyin mulki a wasu kauyukkan Dake karamar hukumar sabon birnin jahar Sokoto.
Yanran Bello Turji da suka hada da Ɗan Bakkwalo, Boka l Tamiske, Hassan Ɗan Kwaro, DOGO da Jammu Baki sun gayyaci mazauna kauyukkan zaman tattaunawa a kauyen Saturu ranar alhamis 04/10/2021.
Yayin Zaman ne suka umurci mazauna kauyen Gangara da su zabi daya daga cikin yan bindigar a matsayin hakiminsu Inda suka zabi dan bindiga Ɗan Bakkwalo a matsayin sabon hakinin gangara.
Nantake sabon hakimin gangara Ɗan Bakkwalo ya gindiya musu sharudda da suka hada da Bude kasuwanni da masallatai da sauransu.
A kauyen Maƙwaruwa Ɗan bidiga Boka Tamisƙe ya nada kanshin a matsayin hakiminsu Inda ya Kira Taron gaggawa da umurtar hakimin garin Mai suna Ɗan Sani da ya gayawa talakkawansa da Kansa cewa yanzu Boka Tamiske ne sabon hakiminsu ba Shiba. Via